Mas'alolin aure Fitowa ta 24(Sheikh Abdulwahhab Abdullah)

Domin neman ƙarin bayani danna nan

TAMBAYA:
Me Sunnah ta tanadarwa
ma’aurata a ranar tarewa?
AMSA:
Abubuwan da sunnah ta kwadaitar
da ma’aurata a ranar tarewa suna
da yawa, amma za mu kawo kadan
daga ciknsu.
1- Da farko, ana so ango ya karbi
amarya da tausasawa, saboda
kasancewarta bakuwa a wannan
ranar. Sannan a ba ta wani abin
sha kamar nono ko madara. Domin
hadisi ya tabbata daga Asma’u bint
Yazid ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﺎ cewa: ranar da
aka kai wa Manzon Allah sallallahu
alaihi wa sallama Nana A’isha ﺭﺿﻲ
ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﺎ ya ba ta nono ta sha. Kamar
yadda muka bayyana a baya.
2- Kuma ana so ango da amarya
su yi sallah raka’a biyu tare a
wannan daren. Kamar yadda ya
tabbata daga Abi Wa’I’ll ya ce:
ﺟﺎﺀ ﺭﺟﻞ ﻣﻦ ﺑﺠﻴﻠﺔ ﺇﻟﻰ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻘﺎﻝ ﺇﻧﻲ ﻗﺪ
ﺗﺰﻭﺟﺖ ﺟﺎﺭﻳﺔ ﺑﻜﺮﺍ ﻭﺇﻧﻲ ﻗﺪ ﺧﺸﻴﺖ ﺃﻥ ﺗﻔﺮﻛﻨﻲ
ﻓﻘﺎﻝ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﺇﻥ ﺍﻹﻟﻒ ﻣﻦ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺇﻥ ﺍﻟﻔﺮﻙ ﻣﻦ
ﺍﻟﺸﻴﻄﺎﻥ ﻟﻴﻜﺮﻩ ﺇﻟﻴﻪ ﻣﺎ ﺃﺣﻞ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﺈﺫﺍ ﺃﺩﺧﻠﺖ ﻋﻠﻴﻚ
ﻓﻤﺮﻫﺎ ﻓﻠﺘﺼﻞ ﺧﻠﻔﻚ ﺭﻛﻌﺘﻴﻦ …
Ma’ana:
Wani mutum ya zo wurin Abdullahi
(Ibn Mas’ud radhiyallahu anhu) sai
ya ce masa: hakika na auri yarinya
budurwa, amma ina jin tsoron kada
mu rabu. Sai Abdullahi Ibn Mas’ud
radhiyallahu anhu ya ce da shi:
Kauna da soyayya daga Allah ne,
sabawa da fitintinu kuma daga
Shaidan ne.
Don haka ranar tarewar ku, ka
umurce ta ku yi sallah raka’a biyu
tare, ita ta tsaya a bayanka …
3- Kuma an so ango ya dora
hannunsa a kan makwarkwadar
amaryarsa sannan ya roki Allah da
addu’ar da ta tabbata daga
Manzon Allah sallallahu alaihi wa
sallam, inda ya ce:
ﺇﺫﺍ ﺗﺰﻭﺝ ﺃﺣﺪﻛﻢ ﺍﻣﺮﺃﺓ ﺃﻭ ﺍﺷﺘﺮﻯ ﺧﺎﺩﻣﺎ ﻓﻠﻴﻘﻞ ﺍﻟﻠﻬﻢ
ﺇﻧﻲ ﺃﺳﺄﻟﻚ ﺧﻴﺮﻫﺎ ﻭﺧﻴﺮ ﻣﺎ ﺟﺒﻠﺘﻬﺎ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺃﻋﻮﺫ ﺑﻚ
ﻣﻦ ﺷﺮﻫﺎ ﻭﺷﺮ ﻣﺎ ﺟﺒﻠﺘﻬﺎ ﻋﻠﻴﻪ .
Ma’ana:
Idan dayanku ya auri mace ko ya
sayi mai yi masa hidima, to, (ya
kama makwarkwadar kanta/sa),
sannan ya ce: Ya Allah ina
rokonKa dukkan alherin da yake
tattare da ita da dukkan alherin da
aka dabi’antar da ita a kan shi,
kuma ina neman tsari a gare ka
daga dukkan sharrin da yake
tattare da ita da dukkun sharrin da
aka dabi’antar da ita a kai .
4- Kuma yana daga cikin abin da
ake so ranar tarewa da sauran
ranaku a yi addu’a yayin saduwa
kamar haka:
ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺟﻨﺒﻨﺎ ﺍﻟﺸﻴﻄﺎﻥ ﻭﺟﻨﺐ ﺍﻟﺸﻴﻄﺎﻥ ﻣﺎ
ﺭﺯﻗﺘﻨﺎ .
Ma’ana
Bismillahi, ya Allah ka nesantar da
mu daga Shaidan kuma ka
nesantar da Shaidan daga abin da
za ka azurtamu da shi (na ‘ya‘ya).
5- An fi so kafin mutum ya kusanci
iyalinsa su yi asuwaki, domin yin
asuwaki sunnar Manzon Allah
sallallahu alaihi wa sallam ne.
Kuma hadisi ya tabbata daga
Mikdam Ibn Shuraih daga Babansa
radhiyallahu anhu ya ce:
ﺳﺄﻟﺖ ﻋﺎﺋﺸﺔ ﻗﻠﺖ ﺑﺄﻯ ﺷﻰﺀ ﻛﺎﻥ ﻳﺒﺪﺃ ﺍﻟﻨﺒﻰ -ﺻﻠﻰ
ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ- ﺇﺫﺍ ﺩﺧﻞ ﺑﻴﺘﻪ ﻗﺎﻟﺖ ﺑﺎﻟﺴﻮﺍﻙ .
Ma’ana:
Na tambayi Nana A’isha ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ
ﻋﻨﻬﺎ cewa: Da mene ne Manzon
Allah sallallahu alaihi wa sallam
yake farawa idan ya shigo
gidansa? Sai ta ce: Yana fara wa
da yin asuwaki.
6- Kuma an fi so ango da amarya
su kasance cikin tsafta wato su
nisanci kazanta tare da sanya
turare.
Haka kuma shari’a ta halatta wa
mutum ya sadu da iyalinsa ta
yadda yake so. Amma ban da
dubura ko kuma yayin da take yin
jinin haila ko biki.
A nan muke nasiha ga mutanen da
suka jarrabtu da saduwa da
iyalinsu ta dubura, ko yayin da
suke jinin haila ko biki, da su
nisanci wannan mummunar dabi`a,
domin babban sabon Allah ne.
Kuma bai halatta ba matan su yi
musu da`a ko da kuwa hakan zai
kai ga rabuwar aurensu.
Amma babu laifi a Shari`ance
ma`aurata su kalli al’aurar junan su
ba tare da wani shamaki ba, domin
hadisan da ake fada cewa, wai
Nana A’isha ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﺎ ta ce:
tunda take ba ta taba ganin
al`aurar Manzon Allah sallallahu
alaihi wa sallama ba, shi ma kuma
bai taba ganin ta ta ba, wannan
kage ne aka yi wa Nana A’isha ﺭﺿﻲ
ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﺎ . Haka kuma akwai wani
littafi da ake kira ‘Kurratul Uyun’
wanda a cikinsa ne ake tattaro irin
wadannan hadisan da ba su
tabbata ba, mafi yawansu ma kage
ne aka yi wa Manzon Allah
sallallahu alaihi wa sallama.
Sannan kuma akwai wani littafi da
ake kira ‘Wasiyyar Annabi
sallallahu alaihi wa sallama ga
Sayyadina Ali radhiyallahu anhu’ a
cikin littafin ana cewa wai Manzon
Allah sallallahu alaihi wa sallama
ya cewa Sayyadina Ali
radhiyallahu kada ka sadu da
matarka a sararin da zaka ga farin
wata ko tauraruwa ko kuma kada
ka sadu da ita face sai ku na
lullube da mayafi. Duk wannan
kage ne aka yi wa Annabi
sallallahu alaihi wa sallama da
Sayyadina Ali radhiyallahu anhu,
wannan bai inganta ba a wurin
malaman hadisi.
7- Shari`a ta hana mace ta ki bayar
da kanta yayin da mijinta ya nemi
ya yi sunna da ita, haka shi ma
mijin yayin da matarsa take
nemansa bai kamata ya ki
sauraronta ba, ba tare da wani
uzuri ba. Domin hadisi ya tabbata
daga Abu Huraira radhiyallahu
anhu ya ce: Manzon Allah
sallallahu alaihi wa sallama ya ce:
ﺇﺫﺍ ﺩﻋﺎ ﺍﻟﺮﺟﻞ ﺍﻣﺮﺃﺗﻪ ﺇﻟﻰ ﻓﺮﺍﺷﻪ ﻓﺄﺑﺖ ﺃﻥ ﺗﺠﻲﺀ
ﻟﻌﻨﺘﻬﺎ ﺍﻟﻤﻼﺋﻜﺔ ﺣﺘﻰ ﺗﺼﺒﺢ
Ma’ana:
Idan mutum ya kira matarsa zuwa
shimfidarsa sai ta ki, to, Mala`iku
za su rika tsine mata har sai gari ya
waye.
8- Haka kuma Shari`a ta hana
ma`aurata su rika fallasa asirin
junansu a wurin kawaye ko abokai.
Misali su rika fadin yadda suke
saduwa da juna da dai sauran
al`amura na sirri da suke gudana a
tsakaninsu. Domin hadisi ya
tabbata Manzon Allah sallallahu
alaihi wa sallama yana cewa:
« ﺇﻥ ﻣﻦ ﺃﺷﺮ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻋﻨﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﻣﻨﺰﻟﺔ ﻳﻮﻡ ﺍﻟﻘﻴﺎﻣﺔ
ﺍﻟﺮﺟﻞ ﻳﻔﻀﻰ ﺇﻟﻰ ﺍﻣﺮﺃﺗﻪ ﻭﺗﻔﻀﻰ ﺇﻟﻴﻪ ﺛﻢ ﻳﻨﺸﺮ
ﺳﺮﻫﺎ ».
Ma’ana:
Hakika yana daga cikin mafi
sharrin mutane a wurin Allah ranar
tashin alkiyama, mutumin da ya
samu sakewa da matarsa, ko kuma
matar ta sake da shi yayin saduwa,
sai ya zo yana bada labari, ko ita ta
je tana ba da labari.
Amma babu laifi ma’aurata su
bayyana abubuwan da suka dace
a shari’a, musanman hukunce-
hukuncen fikihu, da koyar da
rayuwar aure a shari`ance, kamar
yadda matan Manzon Allah
sallallahu alaihi wa sallama suka
rika gayawa sauran mata yadda
suke wanka tare da shi, da sauran
abubuwan da suka shafi
zamantakewarsu ta aure, wannan
ya tabbata a cikin hadisai da da
ma.
FADAKARWA
Yana daga cikin sunnar magabata,
kyautatawa ango da amarya ta
hanyar ba su kyaututtuka na abinci
da sauran abubuwan amfani na
yau da gobe a cikin kwanakin
angwancinsu da bayan tarewarsu,
sai dai kada su kallafawa kansu
abin da ba za su iya ba. Domin
hadisi ya tabbata daga Anas Ibn
Malik radhiyallahu anhu ya ce:
ﻟﻤﺎ ﺗﺰﻭﺝ ﺍﻟﻨﺎﺑﻰ ﺯﻳﻦ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﺎ ﺃﻫﺪﺕ ﻟﻪ ﺃﻡ
ﺳﻠﻴﻢ ﺣﻴﺴﺎ…
Ma’ana:
Yayin da Manzon Allah sallallahu
alaihi wa sallama ya auri Nana
Zainab ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﺎ, sai Nana
Ummu Sulaim ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﺎ ta aika
masa da kyautar abincin da ake
kira Haisan (wanda ya kunshi
dabino da cikwi da kuma mai a
hade)…
Haka kuma yana daga cikin
sunnah a taya ango da amarya
murnar bikinsu tare da yi musu
addu`ar neman zaman lafiya
kamar yadda muka yi bayani a
baya. Ma’ana mutum ya ce da su:
ﺑﺎﺭﻙ ﺍﻟﻠﻪ ﻟﻚ ﻭﺑﺎﺭﻙ ﻋﻠﻴﻚ ﻭﺟﻤﻊ ﺑﻴﻨﻜﻤﺎ ﻓﻲ ﺧﻴﺮ.

3 responses to “Mas'alolin aure Fitowa ta 24(Sheikh Abdulwahhab Abdullah)”
  1. KABIRU UMAR INUWA Avatar
    KABIRU UMAR INUWA

    Assalamu alaikum,
    Madalla da wannan kokari. Allah Ya saka da alkhari, amin summa amin.

  2. alla sakada,,,

  3. Allah ya saka wa malan da gidan aljannah.

Leave a Reply

Latest updates
Categories