Mece ce layya a shari’ance?(Sheikh Abdulwahhab Abdullah)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Mece ce layya a shari’ance?
AMSA: Layya a shari’a, ita ce
yanka dabba daga cikin dabbobin
ni’ima (Bahimatul An’ām, wato:
rakuma da shanu da tumaki da
awaki), tun daga bayan sallar idi
har zuwa faduwar ranar sha uku ga
watan Zul-Hijja, saboda neman
kusanci ga Ubangiji subhanahu wa
ta’ala. Dalili kuwa shi ne: fadinsa
subhanahu wa ta’ala a cikin suratul
Hajj cewa.
ﻟﻴﺸﻬﺪﻭﺍ ﻣﻨﺎﻓﻊ ﻟﻬﻢ ﻭﻳﺬﻛﺮﻭﺍ ﺍﺳﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻲ ﺃﻳﺎﻡ
ﻣﻌﻠﻮﻣﺎﺕ ﻋﻠﻰ ﻣﺎ ﺭﺯﻗﻬﻢ ﻣﻦ ﺑﻬﻴﻤﺔ ﺍﻟﺄﻧﻌﺎﻡ ﻓﻜﻠﻮﺍ
ﻣﻨﻬﺎ ﻭﺃﻃﻌﻤﻮﺍ ﺍﻟﺒﺎﺋﺲ ﺍﻟﻔﻘﻴﺮ (28) ﺍﻟﺤﺞ: ٢٨
Ma’ana:
Domin su halarci abubuwan amfani
(wato ayyukan hajjinsu da yanke-
yankensu), kuma su ambaci sunan
Allah a cikin kwanakin sanannu,
saboda abin da Allah ya azurta su
da shi na daga dabbobin ni’ima…
Haka kuma Abdullahi Ibn Abbās
radhiyallahu anhuma ya fassara
kwanaki sanannu wadanda suka
zo a ayar da ta gabata da cewa
sune
ﺃﻳﺎﻡ ﺍﻟﻌﺸﺮ،
Ma’ana:
Kwanaki goma na farkon Zul-Hijja.
Sannan kuma ya kara da cewa:
ﺃﻥ ﺍﻟﻤﻌﻠﻮﻣﺎﺕ: ﻳﻮﻡ ﺍﻟﻨﺤﺮ ﻭﺛﻼﺛﺔ ﺃﻳﺎﻡ ﺑﻌﺪﻩ .
Ma’ana:
Kwanaki sanannu sune: ranar
layya, da kwanaki uku da suke
bayanta.
Sannan ya ci gaba da cewa:
Hakika Ubangiji subhanahu wa
ta’ala ya sanya wannan lokaci ne
domin ambatonsa.
Haka kuma, hadisi ya tabbata daga
Jubaīru Ibn Mud’īm t ya ce:
Manzon Allah sallallahu alaihi wa
sallama ya ce:
ﻛﻞ ﺃﻳﺎﻡ ﺍﻟﺘﺸﺮﻳﻖ ﺫﺑﺢ .
Ma’ana:
Dukkan ranakun hasken wata
(wato 11 da 12 da 13 ga watan
Zul-Hijjah) ranakun yanka ne.
A kan haka ne kuma magabata
suka tafi, kamar su: Imam Al-Shafi’ī
da Imamul Aūzā’ī da Imam
Hasanul Basrī da Imam Ahmad, da
Imam Mālik da Imam Abū Hanīfah
Allah ya ji kansu baki daya.
Haka kuma, ya tabbata cewa
sahabbai suna yin yanka a cikin
wadannan ranaku.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories