Fatawoyin Rahama By Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo 8th January 2023

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Tambayoyi da Amsoshi da ke ciki tare da Dr. Muhammad Sani Umar R/Lemo, OON

  1. Iyaye da ba musulmi ba su na da haƙƙin aurar da ‘yar su da ta musulma?
  2. Ya hallata iyaye su bawa mutane biyu damar nemar auren ‘yar su?
  3. Ya hallata mutum ya yi walima in ya samu wani ƙarin girma ko wani alheri na duniya?
  4. Ya hallata yaro ya sayar da geron gidansu domin ya biyawa kansa buƙatunsa?
  5. Wanda aka ba shi aikin raba kaya sai kayan ya saura kuma akwai sharaɗi ba a mayar da ragowar kaya?
  6. Ina matsayin a ɗaura mutum a gurbin ma’aikacin da ya rasu?
  7. Ya hallata mutum ya yi ƙarya rashin lafiya domin kada ya je hidimar ƙasa saboda taɓarewa da ake yi!
  8. Ana iya sutra da mutum?
  9. Jini da yake ɗigowa mai shayarwa zai hana ta ibada?
  10. Shin Lukuman Annabi ne?
    Kuma a ina ya rayu?
  11. Ya kamata Ladan in ya makara ya tarar wani ya fara kiran sallah ya karɓi lasfika ya cigaba da ga in da ya tarar?
  12. Hukuncin sanya Hula!
  13. Hukuncin wanda yake aron kuɗin ajiya!
  14. In aka ba mutun kuɗi ya ci abinci in kuɗin ya saura zai iya amfani da sauran kuɗin?
  15. Hukuncin wanda yake tashi daga wajen aiki kafin lokaci amma yana aikin yadda ya kamata!
  16. Ya hallata mutane da suke raba kaya su fifita kawunan su?
  17. Ya hallata mutum ya ba da ‘account numbansa’ ga wani da zai yi amfani da shi don samun tallafin Gwamnati tare da alƙawarin zai bawa mai account din wani abu?
  18. Hukuncin wanda aka ba shi aikin gadi ba ya samun zuwa Sallar Juma’a
  19. Shin Dujjal zuwan sa zai yi tasiri har da waɗanda suka mutu?
    Sannan Yajuju da Annabi Isa a Dujjal -wa zai fara zuwa?
  20. Wanda yake azumin nafila bai samu ikon yi ba saboda rashin lafiya – zai rama?
  21. Shin wanda ya samu tahiya ya samu jam’i?
  22. Ina matsayin yin iƙama da kuskure?
  23. Idan jinin haila ya ɗauke wa mace a lokacin da ba za ta iya wanka ba za ta iya taimama?
  24. Shin haila na iya zuwa bayan kwana 40 da haihuwa?

DOWNLOAD

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories