AIKIN HAJJI A SHARI'ANCE(Ibrahim Jalo Jalingo)

Danna nan domin shiga karatu Online

MAS’ALA TA {1} SHIGA IHRAMI A
JIDDA:
SHIMFIDA:
Ko shakka babu, mas’alar Jidda
Mikati ce ko kuwa ba Mikati ba?
mas’ala ce babba cikin addini
wacce kusan ta shafi dukkan
Musulmi mai yin aikin Hajji ko
Umra, kuma an yi ta fatawowi
dabam-dabam cikinta, wasu sun ce
cikin fatawowinsu kai tsaye: Jidda
Mikati ne, wasu kuwa suka ce kai
tsaye: Jidda ba Mikati ba ne, wasu
kuwa suka bi hanyar rarrabewa
cikin mas’alar. Kuma an sami
Malamai dabam-dabam da suka yi
tali’fi cikin mas’alar, daga cikinsu
akwai wadanda suka yi rubutu mai
fadi da kayatarwa, kamar: Sheik
Adnan Al-Al’uur cikin littafinsa mai
suna: ( ﺃﺩﻟﺔ ﺇﺛﺒﺎﺕ ﺃﻥ ﺟﺪﺓ ﻣﻴﻘﺎﺕ) Watau:
“Hujjojin tabbatar da cewa Jidda
Mikati ne”. Da kuma Dr. Abdullah
As-Sakakir cikin littafinsa mai suna:
( ﻧﻮﺍﺯﻝ ﺍﻟﺤﺞ) Watau Sababbin lamura
da suka taso cikin aikin Hajji”,
Allah Madaukakin Sarki Ya saka
musu da alherinSa. Amen.
MIKATAN DA SUKA TABBATA
CIKIN NASSI:
Akwai mikatai biyar da suka
tabbata cikin nassi, wadannan
Mikatai kuwa su ne: Zulhulaifa, da
Juhfa, da Karna Manazil, da
Yalamlam, da Zatu Irkin, kamar
yadda ya zo cikin Sahihul Bukhari
hadisi na 1524 da Sahihu Muslim
hadisi na 1181 daga Abdullahi Dan
Abbas cewa Annabi mai tsira da
amincin Allah ya sa wa ((Mutanen
Madina mikatin Zulhulaifa,
mutanen Sham kuwa mikatin
Jhufa, Mutanen Najad kuwa
mikatin Karnu Manazil, Mutanen
Yaman kuwa mikatin Yalamlam,
wadannan Mikatai na Mutanen
wuraren da aka ambata ne, da
kuma dukkan mutanen da suka
biyo ta kansu daga cikin wadanda
suka yi nufin aikin Hajji, ko Umra,
mutanen da kuma suke ta cikin
mikatan nan, to ko wannensu zai
dauki harami ne daga inda yake
zaune har ma mutanen Makka za
su dauki harami ne daga cikin
garin Makka)). A wata riwaya ta
Imam Muslim hadisi na 1183 daga
Jabir Dan Abdullahi An ce: ((Wurin
daukan harami na Mutanen Irak shi
ne Zatu Irkin)).
MIKATI NA RESHE
Akwai abin da za mu iya kiran shi:
“MIKATI NA RESHE”, ko “MIKATIN
MUHA’ZAH” watau wurin da yake
seti da mikati mafi kusa da shi,
kuma nisan shi zuwa Makka daidai
yake da nisan wannan Mikati zuwa
Makka, a nan ana nufin mutuminda
ya nufi Makka saboda Umra, ko
Hajji, amma hanyarsa ba ta
biyowa ta kan daya daga cikin
mikatan nan guda biyar da muka
ambata dazu ba, to shi wannan
mutum in ya iso inda yake hannun
riga da mikatai biyu, sai ya duba ya
gani da wani mikati ne cikinsu ya fi
kusa da shi, idan ya gane Mikati
mafi kusan, to, sai ya duba ya ga
nisan nawa ne tsakanin shi
wannan Mikatin da Garin Makka?
In ya san nisan, to, sai ya auna
daga inda yake zuwa Makka nisan
shi ya kai nisan wannan Mikati
zuwa Makkan? In ya kai to sai ya
dauki harami daga wannan wuri
nasa. Saboda wannan wurin a
yanzu sunan shi ya zama “MIKATI
NA RESHE” Misali: mutumin da ya
taso daga Nigeria zuwa Makka
saboda Hajji, ko Umra, in ya iso
Jidda –masalan- sai ya auna ya
gani daga Jidda zuwa Jhufa, da
kuma daga Jidda zuwa Yalamlam,
wanne ne ya fi kusa? In ya fahimci
cewa Jidda ta fi kusa da Yalamlam
a kan Jhufa, to sai ya auna ya gani
daga Yalamlam zuwa Makka kilo
mita nawa ne? Idan ya ga cewa
kilo mita settin ne –masalan- to sai
ya auna daga Jidda kuma zuwa
Makka, in ya tarar kilo mita settin
ne, to sai ya dauki haraminsa daga
Jidda, saboda Jidda a nan ta
zamanto masa “MIKATI NA
RESHE”.
HUKUNCIN DAUKAN HARAMI
KAFIN A KAI MIKATI:
Mas’alar daukan harami kafin a kai
Mikati, watau mutum mai niyyar
aikin Hajji ko Umra tun daga cikin
gidansa, cikin garinsa, ko cikin filin
jirgin sama na kasarsa, ya yi niyyar
yin Hajjinsa ko Umra, ya yi
talbiyya, ya sanya tufafin harami,
ya haramta wa kansa dukkan abin
da ihrami ya haramta masa, har sai
ya gama dawafin umrarsa, ko jifan
jamararsa da yankan hadayarsa.
Wannan mas’ala muhimmiya ce
ainon, saboda in an fahimce ta da
kyau, to, za a iya fita daga
mushkilar Jidda mikati ne, ko kuwa
ba mikati ba ne. Saboda dukkan
maluman Musulunci sun yi ijma’I a
kan cewa duk wanda ya dauki
ihrami na yin Hajji ko Umra kafin
ya kai bigiren Mikati, to ihraminsa
ya inganta, babu kuma wani jini a
kansa, to amma mafi yawan
malamai: Malikiyya, da shafi’iyya,
da Hambaliyya, na kyamar hakan
ba tare da haramtawa ba, su kuwa
Maluman Hanafiyya suna ganin yin
hakan shi mustahabbi. (Dubi
Almugni na Ibn Qudama5/65-66).
Hanafiyya sun ce hakan
mustahabbi ne saboda dogara da
hadisi na 1741 da Abu Dawud ya
ruwaito daga Ummu Salama cewa
Annabi mai tsira da amincin Allah y
ace: ((Wanda ya hurta yin hajji, ko
umra, daga Masallacin Aqsa zuwa
Masallacin Haram, an gafarta
masa abin da ya gabata da abin da
ya yi jinkiri na zunubansa)).
Imamul Albani ya raunana wannan
hadisi kamar yadda ya zo cikin
Dha’ifu Sunani Abi Dawud shafi na
175.
HUKUNCIN RIKON JIDDA A
MATSAYIN MIKATI
Ya ku ‘Yan’uwa Musulmi! Idan mun
fahimci wadanne ne Mikatan nan
guda biyar da suka tabbata cikin
nassi, sannan kuma muka fahimci
abin nan da ake kira “Mikati na
reshe” da kuma “Hukuncin daukan
harami kafin a kai Mikati”? To, ya
dace bayanammu yanzu su dawo
kan jauharin mas’alarmu, wacce ita
ce: Mas’alar hukuncin rikon garin
Jidda a matsayin mikati, ko rashin
rikon shi a matsayin mikati.
Wannan mas’ala a fahimtarmu
tana da bangarori biyu:-
Bangare na farko shi ne: Dukkan
malaman Musulunci sun yi ittifaki
kan cewa garin Jidda mikati ne ga
mutanen da suka rike shi mazauni,
kuma mikati ne ga mutanen da
suke ba mazaunan shi ba ne na
din-din amma sun zo ne domin su
zauna cikinsa na wani dan lokaci,
matukar dai a nan Jiddan ne suka
daura niyyar yin aikin Hajji, ko
Umra. Wannan bigire ijma’I ne
tsakanin Maluman Musulunci.
Bangare na biyu shi ne: Ko
wannan gari na Jidda yana iya
zama mikati ga sauran jama’a
banda wadanda aka ambata a
baya? A nan Malamai sun yi
sabani, sun yi maganganu daidai
har hudu:-
Magana ta farko ita ce: Jidda ba
mikatin kowa ba ne, sai wanda
kawai yake mazaunin garin ne.
Wannan ita ce maganar mafi yawa
daga cikin malamai, hujjarta ita ce
Jidda ba ta daga cikin Mikatan nan
guda biyar da aka ambata a cikin
nassi, kuma ba ta setin daya daga
cikin Mikatan nan guda biyar, ko
kuma mu ce guda biyau, Yalamlam
da Juhfa.
Magana ta biyu ita ce: Jidda mikati
ne ga dukkan wanda ya shigo
garin, ko ta hanyar tudu, ko ta
hanyar teku, ko ta hanyar sama.
Hujjar wannan Magana ita ce:
Jidda reshe ne na Mikati, saboda
yana setin Mikatin Yalamlam.
Wannan shi ne kaulin da Dr.
Abdullahis sakakir ya zaba, kamar
yadda ya zo cikin littafinsa mai
suna Nawazilul Hajji 1/11.
Magana ta uku ita ce: Jidda mikati
ne kawai ga wadanda suka zo
garin ta hanyar teku, ko ta hanyar
sama. Hujjar wannan Magana ita
ce: lalle, Jidda ba ta setin daya
daga cikin Mikatan nan da ake da
su guda biyar, to, amma saboda
lura da aka yi na cewa akwai
tsanani wahala idan har aka dora
wa alhazai daukan harami cikin
jiragen sama, ko cikin jiragen
ruwa, duk kuwa abin da zai jawo
tsanani da wahala ga Al’ummar
Musulmi, to shari’ar Musulunci tana
kauda shi daga gare su, kamar
yadda Allah Madaukakin Sarki Ya
ce cikin Suratul Bakara aya ta 185:
((..Allah Yana nufin sauki gare ku,
ba Ya nufin tsanani gare ku..)).
Kuma Ya ce cikin suratul Ma’ida
aya ta 6 ((..Allah ba Ya nufin sanya
wani kunci a kanku, amma yana
nufin Ya cika ni’imarSa a kanku
tsammanin za ku gode)). Kuma Ya
ce cikin Suratul Hajji aya ta 87
((..Shi ne Ya zabe ku alhalin bai
sanya wani kunci a kanku ba cikin
addini..)).
Magana ta hudu ita ce: Jidda
mikati ne kawai ga mutumin da ya
zo garin ta bangarensa na yamma,
watau kamar mutanen da suka zo
daga kudancin Masar, ko arewacin
Sudan, ko daga Nigeria da
makwabtanta, sawa’un sun zo ne
ta jirgin ruwa, ko kuwa sun zo ne ta
jirgin sama. Hujjar wannan
Magana ita ce: su wadannan da
suka zo ta wannan nahiya ba su bi
ta wani Mikati ba kafin su iso Jidda,
ballantana a kama su da laifin
ketare Mikati kafin daukan harami.
Wannan Magana ta hudu ita ta fi
damun mu, mu mutanen Nigeria.
An sami Maluma da dama da suka
tafi kan wannan mazhaba, daga
cikinsu akwai Babban Malamin nan
na Kasar Saudiyya, watau Sheik
Abdullah Bin Abdurrahman Al-
Jibreen, ga ma abin da yake cewa
cikin littafin Sharhu Umdatil Ahkam
9/35: ((Zai yiwu Jidda ta zamanto
Mikati ga wadanda ke zuwa daga
Sudan, ko daga inda yake seti da
Jidda ta bangaren yamma.
Mutanen Kasar Sudan da abin da
yake seti da ita ba sa bin kan wani
abu daga cikin Mikatan nan da ake
da su, saboda haka idan suka zo
ta jirgin sama, ko suka zo ta jirgin
ruwa bisa ga misali, sai mu ce da
su: Mikatinku shi ne Jidda, amma
wadanda ke zuwa daga Masar, da
Siriya, ko masu kama da su, su
wadannan suna bi ta Mikati kafin
su iso Jidda, suna bi ta kan Juhfa,
ko ta kan Mikatin mutanen Madina
watau Zul-Hulaifa, wadannan ba
ya halatta gare su su ketare
mikatinsu ba tare da sun dauki
harami ba. Saboda wannan
Musulmi sai ya maida hankali
sosai ta yadda ba zai fada cikin
ketare iyaka ba, ta inda ba da jini
zai zama wajibi a kansa)).
Daga cikinsu wadannan Malamai
akwai Sheik Abubakar Mahmud
Gumi daga Nigeria, da Sheik
Mustafa Ahamaduz Zarqaa daga
Jordan, kamar yadda yake rubuce
cikin littafin “Mujallatul Buhuthil
Islamiyya 32/333. Da kuma littafin
Fatawa Islamiyya 2/436. Da Sheik
Abdul Karim Al-Khudhayyir cikin
littafin Sharhu Umdatil ahkam1/23.
FAHIMTAR MAI RUBUTU:
Na amince da Fatawar su: Sheik
Abdullah Bin Abdurrahman Al-
Jibreen, da Sheik Abubakar
Mahmud Gumi, da Sheik Mustafa
Ahamaduz Zarqaa, na cewa: Jidda
mikati ne kawai ga mutumin da ya
zo garin ta bangarensa na yamma:
kamar mutanen kudancin Masar,
da arewacin Sudan, da Nigeria da
makwabtanta. To amma na fi son
Alhazammu da aka san cewa za
su wuce ne kai tsaye zuwa Makka
daga saukarsu Jidda su dauki
haraminsu daga nan gida Nigeria.
Allah Shi ne Ya fi sani, kuma Shi
ne Mai ba da taufiki.
MAS’ALA TA {2} HUKUNCIN
KWANAN MINA CIKIN FILIN
MUZDALIFA:
Dukkan mai kyakkyawan nazari
cikin littattafan Musulunci zai
fahimci cewa wuraren da aka yi
tattalinsu saboda yin aikin ibada,
to, idan bukatar fadada su ta kama,
kamar kuncinsu saboda yawaitar
masu ibada cikinsu, ana iya fadada
su. Saboda abu ne da ya tabbata
cikin littattafan Musulunci cewa
Salafus Salih sun kara fadada
Masallacin Annabi mai tsira da
amincin Allah a lokacin da bukatar
haka ta taso. Khalifa Umar Dan
Khattab Allah Ya kara masa yarda
ya fadada Masallacin Annabi mai
tsira da amincin Allah a shekarar
Hijira ta 17 a inda tsawonsa ya kai
zira’I 130 fadinsa kuma zira’I 120,
sannan Khalifa na uku Uthman
Dan Affan ya fadada shi a shekarar
Hijira ta 29 a inda tsawonsa ya kai
zira’I 160, fadinsa kuwa zira’I 130,
sannan a shekarar Hijira ta 88
Khalifa Amawiy Alwaleed Dan
Abdul Malik ya fadada shi a inda
tsawonsa ya kai zira’I 200, fadinsa
ma zira’I 200, sannan a shekarar
Hijira ta 160 Khalifa Abbasiy Al-
Mahdiy ya fadada shi ta inda ya
kara fadinsa ta bangaren arewa
har na tsawon zira’I 65, sannan a
shekarar Hijra ta 1370, miladiyya
ta 1951, Sarki Abdul Aziz Alu Su’ud
ya fadada shi a inda ya kai
murabba’in mita dubu shida,
sannan a shekarar miladiyya ta
1986 Sarki Fahad Dan Abdul Aziz
ya fadada shi fadadawa mai yawan
gaske ta inda girmansa ta dukkan
bangarorinsa ya kai murabba’in
mita dubu dari hudu. [Dubi Sahihu
Ibni Khuzaimah 2/282, da Tarikhul
Masajidish Shahira 1/42-46].
Kuma Maluman Musulunci sun
bayyana cewa: Hukuncin yin salla
a inda aka kara na Masallacin
Haram da ke Makka, da kuma
Masallacin Annabi mai tsira da
amincin Allah da ke Madina, shi ne
hukuncin yin salla a asalin
Masallatan biyu. Watau karin na
daukan hukuncin abin da aka
karan. Ya zo cikin Littafin Fatawal
Lajnatid Da’imati Lil Buhuthil
ilmiyyati Wal Ifta’I 6/228-229 cewa:-
Tambaya: Shin salla a inda aka
fadada na Masallacin Annabi
karkashin laimomin da aka kafa,
kamar yin salla ne a cikin
Masallacin Annabi?
Amsa: Wuraren da ke shiga cikin
Masallatai bayan an fadada su ana
ba su hukuncin asalin Masallatan
ne, a bisa wannan ana daukar
karin da aka yi a Masallacin
Annabi a ka shigar da shi cikin
Masallacin Annabi hukunce-
hukuncen Masallacin Annabi na
asali na gudana kansa na irin
rubanya lada da wanin haka, koda
yake dai samun lada na bambanta
da juna saboda bambancin da ake
samu cikin ba da sallar, watau cikin
yinta a sahun farko ko a sahu na
biyu, da abin da ya yi kama da
wannan)).
Saboda wannan, a yanzu idan filin
Mina ya yi kunci da matsi ga
mahajjata ta yadda in har ba a
fadada shi ba za su cutu, ke nan ya
zama wajibi a shari’ance a dauki
matakan fadada shi, da yalwata
shi, saboda yin aiki da ka’idodin
Ilmin Qawa’idul Fikhi, kamar ka’idar
nan da take cewa: ( ﺍﻟﻤﺸﻘﺔ ﺗﺠﻠﺐ ﺍﻟﺘﻴﺴﻴﺮ)
watau “Tsanani na jawo
saukakarwa” da kuma wacce take
cewa: ( ﺍﻟﻀﺮﺭ ﻳﺰﺍﻝ) watau: “Ita
cutarwa ana gusar da ita ne” [Dubi
littafin Alwajeez na Dr. Muhammad
Sudqiy shafi na 157,201, da littafin
Alqawa’idul Fiqhiyyah na Ali An-
Nadwiy shafi na 252,265].
Ya zo cikin littafin “Fatawal
Lajnatid Da’imati Lil Buhuthil
Ilmiyyati Wal Ifta’I 11/266 kamar
haka: ((Bigire da kuma zamanin da
ake gabatar da aikin Hajji
abubuwa ne da shari’a ta bayyana
iyakokinsu, babu fagen ijtihadi
cikinsu, kuma Manzon Allah mai
tsira da amincin Allah ya yi aikin
hajji: Hajjin ban kwana ya ce -a
lokacin wannan Hajjin: “Ku koyi
ayyukan hajjinku daga gare ni,
watakila ba zan sake gamuwa da
ku ba bayan wannan shekara
tawa” a wannan Hajjin ya bayyana
iyakokin wuri, da kuma zamani na
aikin Hajji. Iyakokin Mina suna
farawa ne daga kwarin Muhassir
har zuwa Jamratul Aqabah,
saboda haka wajibi ne a kan
wanda ya tafi aikin hajji ya nemi
bigire cikin iyakokin Mina ya
zauna, idan hakan ya gagare shi,
to, sai ya sauka a wani wuri wanda
yake kusa da filin Mina, in ya yi
hakan babu kome a kansa)).
FAHIMTAR MAI RUBUTU:
Na amince da abin da Hukumar
Su’udiyya ta yi na fadada tantunan
Mina har zuwa wani bangare na
filin Muzdalifa, saboda tabbatar da
maslahar Alhazai da tunkude musu
cuta da kunci, amma kuma ina ba
da shawarar cewa abin da ya
kamata Hukumar Su’udiyya ta yi
shi ne: Ta gina benaye a filin Mina
maimakon kakkafa tantuna, a nan
sai ka ga cewa an yi maganin
dukkan cinkoson da ake gani a
Mina yanzu, kuma za ku ga cewa
ko wane alhaji ya sami damar
kwana a asalin filin Mina, ba wai a
filin kari da aka yi saboda maslaha
ba, domin in aka gina benaye za
ku ga cewa filin da aka yi tattalinsa
a da saboda mutanen Nigeria, to, a
lokacinda aka gina benayen
wannan filin sai ya ishi mutanen
Kasashen Pakistan da
Bangaladash da Indiya gaba daya.
Allah Shi ne Mafi sani, kuma Shi
ne Mai ba da taufiki.
MAS’ALA TA {3} HUKUNCIN
JIFAN JAMARAT NA KWANUKAN
TASHRIKI:
SHIMFIDA:
Saboda irin yadda mas’alar: Ko ya
halatta a yi jifar jamarat a cikin
kwanukan tashrik kafin zawalin
rana, ko kuwa bai halatta a yi jifar
ba sai bayan zawali? Saboda
muhimmancinta a wannan zamani
namu, zamanin da mahajjata suka
yawaita ainon, suka kai miliyoyi, ga
kuma irin rashin yelwar filin da ake
yin jifar cikinsa, wanda wannan shi
ya sa ake ta samun hatsura
dabam-dabam lokacin jifar, wasu
lokutan ma abin ya kan kai zuwa
rasa rayukan jama’a da dama,
wannan dalili ya sa an samu da
yawa daga cikin Maluman
Musulunci sun yi ta rubutu kan
wannan mas’ala, saboda samo
hanyar da ya kamata a bi domin
kubutar da Mahajjata daga
wannan mushkila. Daga cikin
Maluman da suka yi rubutu akwai:-
Sheik Abdullah Alhawaliy Ash-
Shamraniy. Inda ya wallafi littafi
mai suna: ( ﺟﺴﺮ ﺍﻟﺠﻤﺮﺍﺕ) watau
Gadar Jamarat.
Da Dr. Sharaf Bin Ali Ash-Shareef.
Inda ya wallafi littafi mai suna: ( ﺭﻣﻲ
ﺍﻟﺠﻤﺮﺍﺕ ﻭﻣﺎ ﻳﺘﻌﻠﻖ ﺑﻪ ﻣﻦ ﺃﺣﻜﺎﻡ) watau
Jifar Jamarat da abin da yake
rataye das hi na hukunce-hukunce.
Da Sheik Abdul Muhsiniz Zaamil,
shi ma ya yi rubutu mai kyau kan
mas’alar, da sauransu. Allah kadai
ke ba da taufiki, She ne kuma
gatan Musulmi.
SABANIN MALAMAI GAME DA
JIFAR JAMARAT KAFIN ZAWALI A
KWANUKAN TASHRIK:
Malaman Musulunci sun yi sabani
kan ingancin yin jifar Jamarat kafin
zawalin rana a cikin kwanaki ukun
nan na tashriki, zuwa maganganu
da dama:-
1. Malikiyya, da Shafi’iyya, da
Hanabila, sun tafi kan cewa: Jifar
Jamarat cikin kwanukan tashriki ba
ya inganta sai in an yi shi bayan
zawali. Hujjarsu a nan ita ce hadisi
na 2635 da Imamu Ahmad ya
ruwaito cikin Musnad4/386 daga
Abdullahi Dan Abbas cewa:
((Manzon Allah mai tsira da
amincin Allah ya yi jifar Jamarat (a
ranakun tashriki) lokacinda rana ta
yi zawali)). Sheik Shu’aibul Arna’ut
ya hassana wannan hadisi cikin
talikinsa a kan Musnadu Ahamad
4/386. Sannan Imamu Muslim ya
ruwaito hadisi na 602 cewa Annabi
mai tsira da amincin Allah ya ce:
((ku koyi ayyukan hajjinku daga
gare ni)). Suka ce abin da za mu
koya a nan shi ne: yin jifar Jamarat
bayan zawali, cikin ranakun
tashriki, domin shi ne Annabi mai
tsira da amincin Allah ya yi.
2. Imam Abu Hanifa ya tafi kan
cewa: yana inganta bayan fitowar
alfijir a yi jifar Jamarat a rana ta
uku kawai na kwanukan tashrik
amma tare da kyamar yin hakan.
Hujjar Abu Hanifa a kan wannan
shi ne: Tunda dai shari’a ta yaddar
wa mahajjata su bar yin jifar ma
gaba daya a ranar tashriki ta uku,
saboda saukake musu wahala, ke
nan ya halatta a saukake musu in
har za su yi jifar a ce: Su yi ta kafin
zawali bayan fitowar alfijir.
3. Tabi’I Tawus Dan Kaisan, da
Tabi’I Ata’u Dan Abi Rabah sun tafi
kan cewa yana halatta a yi jifar
Jamarat a dukkan kwanuka uku na
tashriki. Kuma wannan shi ne
kaulin wasu daga cikin Maluman
Hanabila, kuma akwai riwayar
haka daga Imamu Abi Hanifa.
Hujjarsu a nan ita ce: Abin da
dama aka shar’anta cikin
wadannan kwanaki uku na tashriki
shi ne: Yin jifar Jamrorin nan guda
uku, wanda kuma wannan ba
karamin aiki ba ne, saboda haka
abin da ya fi dacewa da wannan
shi ne: Sai a yalwata lokacin
wannan jifar, ba wai a kuntata shi
ba. Kuma har yanzu muna iya
kiyasta jifar wadannan kwanaki
uku na tashriki a kan jifar ranar
Babbar Salla, mu ce: Ya halatta a
yi jifar Jamarat kafin zawali a cikin
kwanaki uku na tashriki, kamar
yadda ya halatta a yi jifar Jamratul
Aqabah a ranar Babbar Salla kafin
zawali, saboda ko wanne daga
cikinsu jifar Jamarat ne a filin Mina.
Aikin da kuwa Annabi mai tsira da
amincin Allah ya yi na yin jifar
Jamarat a ranaku uku na tashriki
bayan zawali, wannan ya yi shi ne
saboda zaben abin da ya fi yawan
lada ba wai saboda yin sa ya zama
dole ba.
FAHIMTAR MAI RUBUTU:
A bisa ga abin da ya gabata na
maganganun Malamai da
hujjojinsu, lalle ya bayyana mana
a fili cewa yin jifar Jamarat a
ranakun tashriki bayan zawali shi
ne asali, shi ne kuma ya fi karfin
dalili, shi ne kuma mafi yawan
malamai suka yi riko da shi,
wannan shi ya sa ma wanda duk
ya yi haka, an yi ittifaki kan cewa
jifarsa ta inganta, amma wanda ya
yi sabanin hakan wasu malamai
sun ce jifarsa bata inganta ba,
wasu kuwa sun ce jifarsa ta
inganta. To amma duk da wannan,
idan har majibincin lamarin
Musulmi, watau sarkin kasa, ko
shugaban kasa ya yi nazari mai
zurfi game da wannan mas’ala har
ya kai ga fahimtar cewa: Umurtar
alhazai su yi jifar Jamarat cikin
kwanakin tashriki kafin zawalin
rana shi ne zai sama musu
maslaha: maslahar tsare lafiyarsu,
ko tsare dukiyarsu, ko tsare
rayukansu, to a wannan lokaci
wajibi ne al’ummar musulmi masu
aikin hajji su yi masa da’a,
musamman ma idan aka fahimci
cewa: Shi wannan aikin Hajjin fa
dama an gina shi ne a kan
saukake wa mutane, da rashin
kuntata musu. Kamar dai yadda
Imamul Bukhari ya ruwaito hadisi
na 83, da Imamu Muslim hadisi na
1306 daga Sahabi Amru Dan Ass
cewa ((Manzon Allah mai tsira da
amincin Allah a Hajjinsa na
bankwana, ya tsaya saboda
mutane su tambaye shi a filin Mina
a ranar Babbar Salla, sai wani
mutum ya zo masa ya ce: Ban
fadaku ba har na yi aski kafin in
yanka hadayata? Sai ya ce da shi:
Ka yi yankar babu kome, sai wani
mutum ya zo masa ya ce: Ban
fadaku ba har na yanka hadaya
kafin na yi jifar jamrah? Sai ya ce
da shi: Ka yi jifar babu kome.
Watau babu hukuncin wani abu da
aka tamabaye shi wanda ya
kamata a jinkirta, amma kuma aka
gabatar, ko wanda ya kamata a
gabatar, amma kuma aka jinkirta a
wannan ranar face sai ya ce: Ka yi
kawai babu kome)). Wannan hadisi
yana gwada mana cewa fidda
alhazai daga cikin kunci, da masi,
abu ne wanda yake babban
ginshiki cikin aikin Hajjin da Allah
Ya shar’anta wa Al’ummar
Musulmi. Allah Shi ne Mafi sanin
al’amura, kuma Shi ne Mai yi wa
bayinSa taufiki.
MAS’ALA TA {4} HUKUNCIN
LAZIMTAR YIN MAKO GUDA A
MADINA
SHARI’A BATA WAJABTA WA
ALHAJI YIN MAKO GUDA A
MADINA BA
A gaskiya babu inda shari’a ta
wajabta wa alhazai yin mako guda
a garin Madina saboda samun
salloli arba’in cikin jam’I a
Masallacin Annabi mai tsira da
amincin Allah, babu wajibcin haka
cikin Alkur’ani mai girma, ko
Sunnar Annabi mai tsira da
amincin Allah, ko Ijma’in Maluman
Musulunci, saboda wannan, duk
wanda ya wajabta hakan to ya yi
mummunar bidi’a, Allah Ya tsare!
HUJJAR DA WASU KE
AMBATAWA NA YIN HAKAN
A kwai wasu mutane daga cikin
masu wajabta hakan da ke kafa
hujja da hadisi na 12,583 cikin
Musnad na Imam Ahmad 20/40
daga Anas Dan Malik cewa Annabi
mai tsira da amincin Allah ya ce:
((ﻣﻦ ﺻﻠﻰ ﻓﻲ ﻣﺴﺠﺪﻱ ﺃﺭﺑﻌﻴﻦ ﺻﻠﺎﺓ ﻟﺎ ﻳﻔﻮﺗﻪ
ﺻﻠﺎﺓ ﻛﺘﺒﺖ ﻟﻪ ﺑﺮﺍﺀﺓ ﻣﻦ ﺍﻟﻨﺎﺭ ﻭﻧﺠﺎﺓ ﻣﻦ ﺍﻟﻌﺬﺍﺏ
ﻭﺑﺮﺉ ﻣﻦ ﺍﻟﻨﻔﺎﻕ )) Watau: ((Wanda ya yi
salloli arba’in a masallacin nan
nawa ba tare da wata salla ta
kubuce masa ba, to, an rubuta
masa kubuta daga Wuta, da kuma
tsira daga azaba, kuma ya kubuta
daga munafirci)).
AMSAR WANNAN SAI A CE:
Na farko dai: Wannan Hadisi dha’ifi
ne, ba a iya tsaida hujja da irinsa,
saboda cikin isnadinsa akwai wani
mutum majhuli watau wanda ba a
sani ba, shi ne Nubait Dan Umar.
Masanin hadisin nan Sheik
Shu’aibul Arna’ut ya raunana shi
saboda jahalar shi Nubait Dan
Umar, kamar yadda ya zo cikin
hashiyar Musnadu Ahmad 20/40,
haka ma Imamul Albani a cikin
littafinsa na Manasikul Hajj 1/63,
da littafinsa Hajjatun Nabiy1/142.
Sannan shi Imamul Albaniy ya ce
cikin Manasikul Hajji wal
Umra1/63: ((Lazimtar zama mako
guda da masu ziyarar garin
Madina ke yi, domin su sami
damar yin salloli arba’in cikin
masallacin Annabi, saboda a
rubuta musu kubuta daga Wuta da
kuma munafirci (ba daidai ba ne)
saboda hadisin da ke Magana kan
hakan dha’ifi ne ba a kafa hujja da
shi, na bayyana illarsa cikin
Silsilatul Ahadisid Dha’ifa 364, ba
ya halatta a yi aiki da shi, domin
yin hakan shar’anta hukunci ne,
kuma hakan yana iya matsawa
wasu alhazan, kamar yadda na
san hakan da kaina, saboda
tsammanin da suke yi na cewa
hadisin mai inganci ne, sannan
kuma (wani alhajin) na iya rasa yin
wasu sallolin farillan (cikin
Masallacin Annabin) ka ga a
lokacin sai ya shiga cikin kunci
ainon, kuncin da tuni Allah ya raba
shi da shi)).
Na biyu: Koda wannan Hadisn ya
inganta zahirinsa ba ya wajabta wa
alhazai yin mako guda a garin
Madina, domin gayarsa a wannan
lokaci shi ne ya nuna falalar da ke
cikin yin wadannan sallolin ne
kawai, ba tare da cewa wanda ya
kasa yin hakan ya yi wani laifi ba a
shari’a.
Na uku: Hadisi ingantacce da ya zo
cikin wannan babi shi ne hadisi na
241 wanda Imamut Tirmizi ya
ruwaito daga Anas Dan Malik cewa
Annabi mai tsira da amincin Allah
ya ce: (( ﻣﻦ ﺻﻠﻰ ﻟﻠﻪ ﺃﺭﺑﻌﻴﻦ ﻳﻮﻣﺎ ﻓﻲ ﺟﻤﺎﻋﺔ
ﻳﺪﺭﻙ ﺍﻟﺘﻜﺒﻴﺮ ﺍﻷﻭﻟﻰ ﻛﺘﺐ ﺑﺮﺍﺀﺗﺎﻥ، ﺑﺮﺍﺀﺓ ﻣﻦ
ﺍﻟﻨﺎﺭ ﻭﺑﺮﺍﺀﺓ ﻣﻦ ﺍﻟﻨﻔﺎﻕ )) Watau: ((Duk
wanda ya yi salla cikin jam’I
saboda Allah na tsawon kwana
arba’in yana kuma riskar kabbarar
farko, to za a rubuta masa kubuta
biyu: kubuta daga Wuta, da kuma
kubuta daga munafirci)).
Wannan hadisin Imamul Albani ya
inganta shi cikin littafinsa Silsilatul
Ahadisis Sahiha4/629, da kuma
littafinsa Sahihul Jami’is
Sagir2/1089. Kun ga a nan
wannan hadisi sahihi bai kebance
Masallacin Annabi mai tsira da
amincin Allah da wannan falalar
ba, a’a koma a wani masallaci ne
musulmi ya yi wannan aiki na
ibada, to, zai sami wannan falala ta
Allah Madaukakin sarki.
FAHIMTAR MAI RUBUTU:
Da wadannan bayanan da suka
gabata ne za mu iya cewa: in har
alhaji ya sami dama yana iya yin
ko kwana nawa ne a garin Madina,
wannan babu laifi cikinsa, in ya
samu dama yana iya yin wata
guda, ko mako guda, ko kwana
guda, ko yini guda, gwargwadon
dai abin da ya saukaka gare shi ba
tare da lazimtar wani adadi
ayyananne ba, saboda haka a duk
lokacinda shugabannin alhazai
suka ce kwana daya za a yi, to
dayan ne za a yi, in kuma sun ce
biyu, ko uku, ko hudu, ko biyar, ko
shida, ko bakwai, ko fiye da haka,
ko kasa da haka za a yi to hakan
ne za a yi, wannan shi ne
Musulunci, shi ne kuma tabbatar
da maslaha ga mahajjata. Allah Ya
taimake mu, Ya nuna mana
gaskiya gaskiya ce, Ya ba mu ikon
bin ta, Ya nuna mana karya karya
ce Ya ba mu ikon kin ta.
NADEWA:
Mun yi Magana kan ko Jidda mikati
ne, ko kuwa ba mikati ba ne? A
nan mun yarada da fatawar cewa:
Mikati ne kawai ga mutumin da ya
zo garin ta bangarensa na yamma:
kamar mutanen Nigeria, amma
kuma mun fi son Alhazammu da
aka san cewa za su wuce ne kai
tsaye zuwa Makka daga saukarsu
Jidda su dauki haraminsu daga
nan gida Nigeria. Mun kuma
amince da abin da Hukumar
Su’udiyya ta yi na fadada tantunan
Mina har zuwa wani bangare na
Muzdalifa, amma kuma muna ba
da shawarar a gina benaye a Mina
maimakon kakkafa tantuna da za
su kai har wajen Mina. Mun kuma
amince da cewa idan har
shugaban Musulmi, sarki ko
shugaban kasa ya nazarci mas’alar
jifar Jamarat kafin zawali sannan
ya umurci alhazai da yin haka
saboda tsare maslaharsu, to ya
zama wajibi ga mahajjata su yi
masa da’a. Mun kuma amince da
cewa: In har alhaji ya samu dama
yana iya yin ko kwana nawa ne a
garin Madina: yana iya yin mako
guda, ko kasa da haka ko sama da
haka, amma babu inda shari’a ta
wajabta wa alhaji yin mako guda a
garin Madina saboda samun salloli
arba’in cikin jam’I a Masallacin
Annabi mai tsira da amincin Allah,
babu wajibcin haka cikin Alkur’ani,
ko Sunnar Annabi, ko Ijma’in
Maluman Musulunci.
Allah ya Bamu Ikon Yin Aikin Hajji
Karbabbe.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Categories
Latest updates