Fatawoyin Rahama By Dr. Sani Umar Rijiyar Lemo 27th August 2023

Danna nan domin shiga group na karatu Online

TAMBAYOYI

1. Akwai Kaffara ga wadda ake mata Ruƙya ta shaƙe mai yin ruƙyan har ya rasu?

2. Idan mutum ya ci bashi da sharaɗin za a rinƙa cire kuɗin bashin daga albashinsa – sai aka kore shi bayan an cire na wata ɗaya-shin bashin ya faɗi akansa?

3. Ya hallata Mutum(ƙwarraren likita) da yake aiki a Asibitin Gwamnati sannan ya samu wani aiki a wata ƙungiyar da bata Gwamnati ba (NGO)- ya nemi wani abokinsa (ƙwarraren likita) ya rinƙa yin aikin da aka ɗauke shi, shi kuma ya tafi na ƙungiyar?

4. Akwai zakka ga mai ɗaukar Albashi?

5. Ya ya ingancin sallar Limamin da ya yi Sujjada ɗaya maimakon biyu saboda mantuwa?

6. Shin azumtar watan Rajab, Sha’aban da Shawwaal ya na da asali?

7. Hukuncin ruwan da najasa ta shiga cikinsa?

8. Hukuncin wanda ya bi jam’in Sallar la’asar alhali ya shiga da niyar Sallar Azahar?

9. Hukuncin ƙwan da aka ciro daga Kazar da ta mutu!

10. Ya hallata sanya sunan Mala’iku kamar *Munkar* da *Nakir*?

11. Hukuncin mace da ta bawa ‘ya’yanta maganin bacci suka sha sai suka mutu!

12. Hukuncin wanda ya bi Limamin da yake sallar Isha a zatonsa Sallar Magriba Limamin yake yi!

13. Ya hallata mutumin da yake sana’a ya yi ƙaryar bashi da wasu kayan gyra domin masu kawo gyra su bashi kuɗin motar sayo kayayyaki alhali yana da kayayyakin?

14. Adduar da za a yiwa iyayen da suka rasa yaro ƙarami!

15. Ya hallata mutum yayi salla shi kaɗai in yana ma’aikatar da ake rufe ƙofofi da daddare har zuwa safe!

16. Ya hallata wanda ya je cin kasuwa ya yi ƙasaru!

17. Me ya kamata mutum ya yi in yaje massalacin Jumu’a da wuri?
Nafila da yawa ko Karatu ko Azkar

18. A wanne lokaci mutum ya kamata ya yi addua – bayan kiran Sallar farko ko kiran Sallah na biyu?

19. Ya hallata wani Liman daban ya sallaci sallar Isha’i wanda ba shi ne ya sallaci sallar Magriba in an haɗa Magriba da Isha’?

20. Masbukai da suka fara Sallah sai suka ankara Limami yana gyaran sallah, za su iya ƙatse sallarsu su bi Limamin?

21. Ibadar wanda ba ya iya riƙe bawali (Fitsari)

22. Hukuncin mutum ya siyar da jininsa!

23. Hukuncin wanda ya kashe kansa saboda nauyin bashin da ake bin sa.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories