2018 Ramadan Tafseer By Dr. Idrees AbdulAzeez Bauchi(Night)
Wanene Khalifar Annabi Na Farko? Muqabala Tsakanin Sh. Musa Yusuf Asadussunnah da AbdulJaleel Dan Shi'ah
كتاب: ألفية السيوطي في علم الحديث
Khudbah: Ka tsaya inda aka umarceka
كتاب: موقف الأزهر من الشيعة الاثني عشرية
Muhadara: Rahamar Annabi By Dr. Sani Umar
Ma'anar Cewa Allah Ya Halicci Annabi Adam A Surar Sa
Assalamu Alaikum warahmatullah.
Bukhari Da Muslim sun riwaito daga Abi Huraira(Radiyallahu Anhu) Manzon Allah(Sallallahu Alaihi Wasallam) yace:
عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ عَنْ النَّبِيِّ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ : خَلَقَ اللَّهُ آدَمَ عَلَى صُورَتِهِ طُولُهُ سِتُّونَ ذِرَاعًا فَلَمَّا خَلَقَهُ قَالَ اذْهَبْ فَسَلِّمْ عَلَى أُولَئِكَ النَّفَرِ مِنْ الْمَلائِكَةِ جُلُوسٌ فَاسْتَمِعْ مَا يُحَيُّونَكَ فَإِنَّهَا تَحِيَّتُكَ وَتَحِيَّةُ ذُرِّيَّتِكَ فَقَالَ السَّلامُ عَلَيْكُمْ فَقَالُوا السَّلامُ عَلَيْكَ وَرَحْمَةُ اللَّهِ فَزَادُوهُ وَرَحْمَةُ اللَّهِ فَكُلُّ مَنْ يَدْخُلُ الْجَنَّةَ عَلَى صُورَةِ آدَمَ فَلَمْ يَزَلْ الْخَلْقُ يَنْقُصُ بَعْدُ حَتَّى الآن
“Allah ya halicci Adam(Alaihissalam) a bisa surarsa, yana da tsawon zira’i sittin, bayan da Allah ya halicceshi sai yace masa ka tafi kayi sallama zuwa ga wa’incan jama’a na mala’iku wanda suke zaune, sannan ka saurari abinda zasu gaisheka dashi, domin itace gaisuwarka da zuri’arka, Sai Annabi Adam(Alaihissalam) yace “Assalamu Alaikum” Sai suka ce masa “Assalamu Alaika Warahmatullah” sai suka masa karin “warahmatullah” Duk wanda zai shiga Aljannah zai shiga ne a surar Adam, Halitta bai bar raguwa ba(ma’ana tsawonsu) har zuwa yanzu.
Bukhari:6227
Muslim:2841