Idan Ka zabi mace mai addini ka aura ka rabauta

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Da sunan Allah mai rahama mai jin kai.

Kowani na miji akwai abinda yake jan hankalinsa wurin auren mace, mafi shahara daga cikin wa’innan sabuba sune kamar haka:

  • Kyawu
  • Dukiya
  • Dangi
  • Addini

Wa’innan abubuwa sune mafi yawan abubu wa da suke jawo hankalin na miji ya auri mace.

Shi yasa Annabi Sallallahu alaihi wasallama ya zaba mana abinda yafi daga cikin wa’innan abubuwa guda hudu, shine addini.

Annabi Sallallahu alaihi wasallama yace

تنكح المرأة لأربع‏:‏ لمالها، ولحسبها، ولجمالها، ولدينها، فاظفر بذات الدين تربت يداك

Ana auran mace dun abubuwa guda hudu.

Dukiyarta, danginta, kyawunta, addininta. Ka zabi mai addini Ka rabauta.

Bukhari: 5090
Muslim: 1466

Babu laifi mutum ya auri mace kyakkyawa, ko mai dukiya amma ta zamto tana da addini, domin inka auri mara addini Ba zai tsaya akanta ba, har yaranka da zata haifa maka zai shafa.

Hakanan ba wai ana nufin mai addini itace wacce ta haddace Al-Qur’ani ko hadisai ba. A’a abinda ake nufi ta zamto in ance mata Allah yace Annabi yace zata bi koda ko bata da ilimi mai zurfi.

Allah yasa mudace

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories